Labarai
Majalisar Dattawa ta fara nazari kan ƙudirin gyaran dokar zaɓe

Majalisar dattawa ta fara nazari kan ƙudirin gyara dokar zaɓen shekara ta 2022, inda ta mayar da hankali kan wasu sassa da ake ganin suna buƙatar ƙarin gyara domin inganta zaɓe a ƙasar nan.
Ƴan majalisar sun yi hakan ne ta hanyar fara nazarin wasu takardu da gyare-gyaren da shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Harkokin Zaɓe, Sanata Simon Lalong, ya gabatar, kafin a ci gaba da muhawara a bainar jama’a.
Ƙudirin ya ƙunshi batutuwa kamar hana yin rajista a jam’iyyun siyasa fiye da ɗaya da daƙile sauya sheƙa bayan zaɓen fidda gwanida da kuma tanadin hukunci ga masu karya doka.
A zaman majalisar na yau Alhamis, ‘yan majalisar sun amince da buƙatar janye wasu sassan ƙudirin da aka riga aka amince da su a watan Disambar 2025, domin a sake duba su.
Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya jaddada muhimmancin yin nazari mai zurfi kan ƙudirin, duk da cewa Majalisar Wakilai ta riga ta amince da shi, yana mai cewa, dokar na da matuƙar muhimmanci musamman yayin da ake shirin zaɓen shekara ta 2027, don haka kamata ya yi, a yi taka-tsantsan domin kauce wa rikice-rikicen shari’a bayan zaɓe.
You must be logged in to post a comment Login