Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar dinkin duniya ta ce fiye da mutane miliyan daya ke mutuwa dalilin cutar tarin fuka

Published

on

Majalisar dinkin duniya ta ce; mutane miliyan daya da dubu dari shida ne suke mutuwa duk shekara a dalilin cutar tarin fuka.

 

Ta kuma ce ba ya ga rasa rayukan, cutar za ta kuma janyo wa duniya asarar kudade dala tiriliyan daya kafin nan zuwa shekarar dubu biyu da talatin.

 

Sakatare Janar na majalisar dinkin duniya Antonio Guterres ne ya bayyana haka, yayin wata ganawa da ya yi da wasu kungiyoyi masu zaman kansu a shalkwatar hukumar da ke birnin New York din kasar Amurka.

 

Ya ce dole ne al’ummar duniya su dunkule waje guda domin yakar cutar tarin fuka.

 

Sai dai ya ce; ba za a samu nasara ba matukar ba a dakile dalilan da suke ta’azzara cutar ba musamman talauci.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!