Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hatsaniya ta barke a majalisar dattawa

Published

on

Hatsaniya ta barke a majalisar dattawa a jiya biyo bayan gabatar da sakamakon rahoton kwamitin kula da hukumar zabe ta kasa INEC kan tantance mutanen da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya turo da sunayensu don nadasu a matsayin kwamishinoni a hukumar INEC.

 

Hatsaniyar ta fara ne lokacin da shugaban kwamitin Sanata Nazifi Gamawa, ya gabatar da sakamakon rahoton; inda ya bayyana cewa kwamitin bai amince a nada wakilin jihar Zamfara Ahmad Bello Mahmud don zama kwamishina a hukumar ta INEC ba.

 

Kammala jawabinsa ke da wuya, sai Sanata mai wakiltar mazabar Zamfara ta Tsakiya Kabiru Marafa, ya mike ya kuma zargi mambobin kwamitin da karbar cin hanci.

 

Ya ce yana da kwararan hujjoji da suka tabbatar masa cewa mambobin kwamitin sun karbi na goro daga wajen wasu mutane don kin amincewa da wakilin na jihar Zamfara.

 

Sanata Kabiru Marafa ya ma fito karara ya zargi gwamnan jihar ta Zamfara Abdul’aziz Yari da hannu dumu-dumu wajen baiwa mambobin kwamitin cin hanci don dakile yunkurin tantance Ahmed Bello Mahmud zama kwamishina a hukumar ta INEC.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!