Connect with us

Labarai

Majalisar wakilai ta ɗage ranar komawa daga hutu

Published

on

Majalisar Wakilai Najeriya, ta ɗage ranar komawa hutu daga 23 ga Satumba zuwa 7 ga Oktoba, duk da cewar  kwamitoci za su ci gaba da gudanar da ayyukan su.

Hakan  na ƙunshe ne a cikin wata sanawa da majalisar ta aikewa  dukkan ‘yan majalisar, inda ta yi kira da su sake shirye-shiryen su da tsare-tsaren su domin su yi daidai da canjin da aka samu.

Ta cikin sanarwar shugaban Majalisar Wakilai, Abbas Tajudeen, ya ce yana yi ‘yan Najeriya albishir cewa majalisar za ta hanzarta amincewa da dokar gyaran kundin tsarin mulki na 1999.

Mataimakin shugaban majalisar, Benjamin Kalu, wanda shi ne shugaban kwamitin gyara kundin tsarin mulki, ya ce za a gudanar da tsarin cikin haɗin kai da ba kowane ɓangare dama domin tabbatar da cewa kowa ya samu damar shiga cikin lamarin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!