Connect with us

Labarai

Majalisar wakilai ta buƙaci gwamnatin tarayya ta jingine aiwatar da sabuwar dokar haraji

Published

on

Majalisar wakilai ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta jingine shirinta na fara aiwatar da sabuwar dokar haraji mai cike da ce-ce-ku-ce da ruɗani, har sai an kammala bincike kan zargin sauya wasu daga cikin dokokin da majalisar ta amince da su.

 

Ɓangaren marasa rinjaye a majalisar sun bayyana bukatar dakatar da aiwatar da sabuwar dokar haraji domin gudanar da bincike mai inganci, wanda majalisar ta kafa don gano gaskiyar batun.

 

Wannan kiran ya biyo bayan zargin cewa an sauya wasu sassa na dokokin haraji bayan da majalisar ta amince da su, wanda hakan ya janyo mummunan ruɗani a tsakanin sassan gwamnati.

 

A halin yanzu, ɗaya daga cikin shugabannin majalisar, ya bayyana cewa akwai bukatar a tabbatar da gaskiyar wannan al’amari kafin a ci gaba da aiwatar da dokar.

 

Duk da haka, ɓangaren gwamnatin ya nesanta kansa daga zargin, inda ministan yaɗa labarai, Mohammed Idris, ya bayyana cewa sabuwar dokar haraji za ta fara aiki a ranar 1 ga Janairun, 2026 mai kamawa, kuma akwai haɗin kai tsakanin gwamnati da majalisar kan wannan lamari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!