Connect with us

Labarai

Mazauna Durumin Iya sun yi taron shirin gudanar da aikin gayya

Published

on

Mazauna unguwar Durumin Iya da ke yankin ƙaramar hukumar Birni ta Jihar Kano, sun gudanar da taro domin tsara yadda za su gudanar da aikin gayya domin magance barazanar ambaliyar ruwa a daminar bana.

 

Mai unguwar yankin na Durumin Iya, Malam Jamilu Umar, ne ya bayyana hakan yayin ganawarsa da manema labarai.

 

Mai unguwar, ya ce, taron ya samu halartar matasa da dattijan unguwar, inda aka cimma matsaya kan tattara kuɗaɗe da haɗa hannu domin shawo kan ambaliyar da ke barazana yayin da Damina ke ƙara kankama.

 

Malam Jamilu Umar, ya nuna farin cikinsa kan yadda al’umma suka haɗu waje guda, tare da yin kira ga shugabanni su mara wa shirin nasu baya.

 

Za dai a gudanar da aikin gayyar ne a ranar Lahadi mai zuwa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!