Labarai
MDD ta kaddamar da neman taimako domin tallafawa Sudan

Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya tare da ƙungiyoyi abokan hulɗa 123 sun ƙaddamar da neman gudummawar sama da dala biliyan 1, domin taimaka wa miliyoyin yan ƙasar Sudan da suka tsere daga ƙasar su da yaki ya dai dai ta.
Wannan na da nufin kai agajin gaggawa ga ‘yan Sudan miliyan 5, da ke gudun hijira a ƙasashe bakwai makwabta da suka hada da Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya da Chadi da Masar da Habasha da Libyia da Sudan ta Kudu da Uganda.
Daraktan yankin Gabas da Kudancin Afirka na hukumar, Mamadou Dian Balde, ya shaida wa manema labarai a Geneva cewa rikicin Sudan shi ne mafi girma da ya raba jama’a da muhallan su a duniya a yanzu.
Ya buƙaci ƙasashen duniya su ƙara tallafin kuɗi domin hana ƙara tabarbarewar rayuwar iyalan da rikicin ya raba da muhallan su.
You must be logged in to post a comment Login