Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mun kama masu Garkuwa da mutane da barayin baburan – Dikko

Published

on

Rundunar yan sandan jihar Kano ta yi holin wasu mutane da ta kama bisa zargin laifin fashi da makami tare da garkuwa da mutane.

Baya ga wannan ma ana zargin mutanen da satar motoci da baburan Adaidaita sahu da babura masu kafa biyu sai Kuma masu safarar miyagun kwayoyi.

Kwamishinan yan sandan Kano Samaila Shu’aibu Dikko ne ya tabbatar da hakan a zantawarsa da Freedom Radio.

Ya ce mutanen da aka kama an same su da bindigogi da magungunan da amfaninsu ya kare.

Dikko ya yabawa jami’an tsaro da yan jaridu bisa gudunmawar da suke bayarwa, inda ya tabbatar da cewa da zarar an kammala bincike za a tura su kotu don a yanke musu hukunci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!