Connect with us

Labarai

Mun kusa kawo karshen rikicin cikin gida a PDP – Turaki

Published

on

Daya daga cikin bangarorin jam’iyyar PDP karkashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki ya tabbatar da fara sabon yunkurin sulhu domin hada kan bangarorin da ke rikici a cikin jam’iyyar.

A wata sanarwa da ya sanya wa hannu da kansa, Turaki ya ce shugabannin jam’iyyar na nazarin hanyoyi daban-daban da za su kai ga samun dawwamammen zaman lafiya a cikin PDP.

Ya bayyana cewa wannan mataki na zuwa ne a daidai lokacin da ake kokarin rage sabani da rarrabuwar kawuna da suka dabaibaye jam’iyyar a ‘yan kwanakin nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!