Labarai
Mun samar wa maniyyata 1,010 Visa- Gwamnatin Yobe

Hukumar kula da jin dadin alhazai ta Jihar Yobe, ta bayyana cewa, ta yi wa maniyyata dubu daya da goma Bizar shiga kasar Saudiyya domin gudanar da aikin Hajjin bana cikin maniyyatan jihar dubu daya da casa’in da hudu.
Shugaban hukumar Alhaji Mai Aliyu Usman, ne ya bayyana hakan a zantawarsa da wakilinmu Abdulkarim Muhammad Abdulkarim.
Shugaban, ya yi karin bayani game da shirin su na tunkarar ibadar aikin Hajjin mai zuwa, inda ya bayyana cewa, sun kuma tanadi Dalolin Amurka da za su bai wa kowane maniyyaci kudin guzuri domin shirin gudanar da aikin Hajji bana.
Alhaji Mai Aliyu Usman, ya kara da cewa, sun sayi Dalar ne daga wani kamfanin canjin kudaden ketare, inda za su bai wa kowanne maniyyaci Dala 500.
You must be logged in to post a comment Login