Connect with us

Labarai

Mutane 14 sun mutu bayan hadarin jirgin ruwa

Published

on

Mutane 14 da suka hada da mata da wani ƙaramin yaro sun rasu sakamakon haɗarin jirgin ruwa a yankin Gumbi da ke Karamar Hukumar Yawuri a jihar Kebbi.

 

Lamarin ya faru ne bayan magariba, inda irgin ruwan da ke ɗauke da mutane sama da 70 ya rabe gida biyu a hanyar sa ta dawowa daga kai amarya a yankin Karamar Hukumar Ngaski.

 

Alʼummar yankin sun ce wadan da suka rasun mata ne, sai kuma wani ƙaramin yaro guda ɗaya.

 

Masu aikin ceto sun ce sun samu nasarar ceto sauran mutanen da ke cikin jirgin, yayin da ake ci gaba da tattara bayanai kan musabbabin haɗarin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!