Connect with us

Labarai

Mutane 20 sun rasu sakamakon kifewar jirgin ruwa

Published

on

Mutane 20 sun rasu  yayin da aka ceto 13 da sakamakon kifewar wani jirgin ruwa da ya tashi daga Adiyani a Karamar Hukumar Guri ta Jihar Jigawa zuwa Nguru a Jihar Yobe.

‎Wani  shaidar gani da ido mazaunin garin Nguru ya bayyana cewa, har yanzu ana ci gaba da neman wasu mutane 15 da ake zargin sun nutse cikin ruwan, yayin da jami’ai  ke gudanar da ayyukan ceto da bincike a yankin.

‎Hatsarin, wanda ya faru da misalin karfe 7 na daren  jiya Asabar, ya jefa al’ummar yankin cikin jimami, yayin da mazauna ke bai wa jami’an ceto goyon baya a kokarin gano sauran mutanen da ake fatan cetowa ko gano gawarwaki.

Mazauna yankin na ci gaba da zaman dar da  damuwa da rashin tabbas game da wasu ‘yan uwansu da ke cikin jirgin, yayin da hukumomi suka yi kira ga jama’a da su kiyaye hanyoyin ruwa da bin ka’idojin Tuki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!