Connect with us

Labarai

Najeriya ƙasa ce mai mutunta bambancin addinai- Tinubu

Published

on

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa Najeriya ƙasa ce mai mutunta bambancin addinai, tare da kare ‘yan ƙasar ba tare da nuna wariya ba.

Shugaba Tinubu, ya bayyana hakan ne ta cikin martaninsa bisa kalaman Shugaban Amurka Donald Trump, wanda ya zargi Najeriya da rashin kare addinai. Tinubu ya ce gwamnatin sa na ci gaba da aiki tuƙuru don tabbatar da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin musulmai da kiristoci a faɗin ƙasar.

Haka kuma, Tinubu, ya jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da aiwatar da manufofi na haɗin kai, adalci da kariya ga kowa da kowa bisa tsarin doka domin tabbatar da cewa Najeriya ta zauna cikin zaman lafiya da ɗorewar cigaba.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!