Connect with us

Labarai

Nasiru Yusuf Gawuna ya yi murabus daga mukaminsa na Shugaban Hukumar FMBN

Published

on

Tsohon ɗan takarar gwamna a Kano a Jam’iyyar APC na shekarar 2023, Nasiru Yusuf Gawuna, ya yi murabus daga mukaminsa na Shugaban Hukumar Gudanarwa  Bankin bada lamunin  Gidaje na Tarayya FMBN.

 

A cikin wata takardar murabus mai ɗauke da kwanan watan 27 ga Maris, 2026, Gawuna ya ce matakin nasa ya fara aiki nan take, yana mai cewa ya yi hakan ne domin bin umarnin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, na bukatar masu rike da mukaman siyasa su sauka bisa tanade-tanaden dokar zabe.

 

Gawuna ya kuma gode wa Shugaba Tinubu bisa damar da ya ba shi na yin hidima, yana mai cewa mukamin ya ba shi damar bayar da gudunmawa ga ci gaban bankin da kuma kasa baki daya.

 

Ya kara da cewa zai tabbatar da mika ragamar aiki cikin tsari, bisa ka’idoji da dokokin da suka dace.

 

Saukar ta sa na zuwa ne da wasu  rahotanni ke  nuni da cewa Gawuna na shirin sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa ADC, bayan tattaunawa da tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, duk da babu  sanarwa a hukumance kan hakan zuwa yanzu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!