Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Karya tsarin dimukraɗiyya shi ne tushen matsalar siyasa – Ɗantiye

Published

on

Tsohon ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Garki da Ɓaɓura Nasir garba Ɗantiye ya ce, ƴan Najeriya sun yi hannun riga da tsarin dimukraɗiyya shiyasa har yanzu ba’a samu ci gaba a ɓangaren siyasa ba.

Ɗantiye ya kuma ce ba’a gudanar da sahihan zaɓe shiyasa ake samun baragurbin shugabanni a ƙasar.

Nasir garba Ɗantiye ya bayyana hakan ta cikin shirin Barka da Hantsi na Freedom Radio.

“Na ƙalubalanci dukkanin jam’iyyu su fito su ce suna bin tsari da dokokin yadda aka tsara jam’iyyunsu da kuma dimukraɗiyya.”

“Ana samun rigingimun cikin jam’iyya ne saboda ba’a bin abinda dokar jam’iyya ta ce sai abinda iyayen gida suka ce.”

Nasir Garba ya kuma ce babu amana a tsakanin 6an siyasa shiyasa ba’a yin abinda ya dace, kazalika idan mutane suka san haƙƙinsu akan shuwagabanni to za’a samu sauyi a siyasar Najeriya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!