Connect with us

Labarai

Rashin hukunta masu laifi na kara ta’azzara matsalar tsaro: Gwamnatin Bauchi

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa ta koka bisa ga yadda hukumomi ke sakin mutanen da aka samu da laifin satar na’u’rorin dake samar da Ruwa a jihar.

Kwamishin ma’aikatar Ruwa na jihar Ibrahim Garba Hannun Giwa ne ya bayyana hakan a zantawarsa da Freedom Radio.

Kwamishinan ya kara da cewa ‘jami’an tsaro a jihar sun sha kama wadanda ake zargi suna sacewa hukumar kayayyakin a kananan hukumomin Kazaure da Ringim da kuma Dutse da garin Shuwarin ta karamar hukumar Kiyawa, amma daga baya sai aka sake su’.

Haka kuma ya kara da cewa irin wannan sace-sace da rashin hukunta masu yi shi ke haifar da cikas a yunkurin gwamnatin jihar na Samar da Ruwa mai tsafta cikin sauki ga al’ummar jihar.

Rahoton: Adulkadir Haladu Kiyawa

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!