Connect with us

Labarai

Rundunar sojin Najeriya sun hallaka jagoran ’yan bindiga Kachalla Kallamu

Published

on

Rundunar Battaliyan Sojoji na 8 Division a kasar nan sun kashe shahararren jagoran ’yan bindiga, Kachalla Kallamu, a ƙaramar hukumar Sabon Birni ta jihar Sokoto kamar yadda Wani majiyar jami’an tsaro ya bayyanawa kamfanin dillancin labarai ta kasa NAN

 

Majiyar ta ce Kallamu, wanda shakiki ne ga shahararren jagoran ’yan bindiga, Bello Turji, an kashe shi ne tare da haɗin gwiwar ’yan sa-kai a yankin, a wani samame na musamman da sojojin Nigeria Army suka gudanar a ƙauyen Karawa da safiyar ranar Litinin.

 

Rahoton ya kara da cewa Kallamu, wanda ya fito daga Garin-Idi a Sabon Birni, ya jima yana addabar al’ummomin yankin, kuma kwanan nan ya dawo daga jihar Kogi bayan ya gudu sakamakon farmakin sojoji a watan Yuni 2025, inda aka ce ya nemi mafaka.

 

Mai ba Gwamnan Jihar shawar kan tsaro kanal Ahmad Usman mai ritaya, da wasu mazauna jihar sun yabawa Sojojin Najeriya kan nasarorin da suka samu a yaki da ’yan bindigar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!