Connect with us

Labarai

Rundunar Sojin Najeriya ta yabawa dakarunta bisa dakile harin ‘yan ta’adda a Jihar Kano

Published

on

Babban kwamandan sojojin Najeriya na runduna ta daya sashen  Operation Fansar Yamma Manjo Janar Abubakar Wase, ya yabawa dakarun sojin bisa yadda suka nuna kwarewa da jajircewa wajen dakile harin ‘yan ta’adda a Karamar Hukumar Shanono dake jihar Kano.

Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da mataimakin mai magana da yawun rundunar Caftin Babatunde Zubairu ya rabawa manema labari bayan ziyarar da rundunar ta kai yankin Farin Ruwa da Tsaure na garin Shanono a Jihar Kano.

Sanarwar ta ce, babban kwamandan yayi kira ga dakarun nata da su ci gaba da jajircewa wajen ganin suna aikinsu yadda ya kamata, don ganin sun yaki ta’addanci a Jihar Kano.

Haka zalika sanarwar ta ce duba da yankin Shanono yana tsakanin Bodar Kano da Katsina da ke Arewacin Najeria, ya sanya wurin ya zama yankin da ‘yan ta’adda suke addaba a yanzu, don haka yake kira ga dakarun da su sanya idanu sosai, da hadin gwiwar sauran jami’an tsaro don yakar matsalar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!