Connect with us

Labarai

Rundunar soji a Najeriya sun kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su a jihar Kogi

Published

on

Dakarun runduna ta 12 ta sojojin kasar nan sun fatattaki ‘yan bindiga tare da kubutar da wasu mutane da aka yi garkuwa da su a wani samame da suka kai a hanyar Oshokoshoko zuwa Obajana a karamar hukumar Lokoja a jihar Kogi.

Wata sanarwa da mukaddashin daraktan hulda da jama’a na rundunar sojin ta 12 Laftanar Hassan Abdulahi ya fitar a safiyar yau Laraba, ta ce, farmakin na daga cikin kokarin da ake yi na yaki da ‘yan fashi masu garkuwa da mutane da sauran munanan laifuka a fadin jihar.

Ya ce, a safiyar jiya Talata ne dakarun suka kai farmakin bayan sahihan bayanai kan yadda ‘yan bindiga suka sace wasu mutane tare da tserewa da su a kan titin Oshokoshoko zuwa Obajana inda nan take dakarun sojin da ke sansanin sintiri na Kabba, tare da hadin gwiwar wasu rundunonin hadaka, suka gudanar da wani samame na musamman domin kame bata garin.

Haka kuma, ya kara da cewa, yayin harin an kwato bindiga kirar AK-47 guda daya da kuma ceto wani da aka yi garkuwa da shi

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!