Connect with us

Labarai

Rundunar ‘yan sanda ta tura Jami’ai kasuwanni da kan iyakoki a Bauchi

Published

on

‎Rundunar ‘yan sandan Jihar Bauchi ta ce ta ƙara ƙaimi wajen ƙarfafa tsaro domin daƙile ayyukan ‘yan bindiga da sauran laifuka a jihar.

‎Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Sani Omolori Aliyu, ya bayyana cewa sun ƙara tura jami’ai a kasuwanni, tashoshin mota da kuma yankunan kan iyaka domin tattara bayanan sirri da kuma ɗaukar matakan tsaro kafin aukuwar laifi.

Wannan ‎matakin dai ya biyo bayan umarnin Sufeto Janar na ‘yan sanda, Olatunji Rilwan Disu, ya bayar na mayar da hankali kan aikin ‘yan sanda na zamani da zai dogara kan bayanan sirri a faɗin ƙasar nan

‎Haka kuma rundunar ta ce tana ƙara kusantar al’umma ta hanyar tarurruka da kuma wayar da kan jama’a kan yadda za su gane barazana da kuma hanyoyin neman agajin gaggawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!