Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Rundunar ‘yan sanda za ta girke jami’anat a ofisoshin hukumar INEC

Published

on

Mai rikon mukamin Sifeto janar na ‘yan sandan Najeriya Muhammed Adamu, ya bada umarnin rarraba ‘yan sanda a ofisoshin hukumar zaben mai zaman kanta ta kasa INEC da ke fadin kasar domin tabbatar da tsaro a yayin babban zaben da ke tafe.

Muhammed Adamu ya kuma ce, ya zama wajibi duk wasu kwamishinonin ‘yan sanda da ke fadin Najeriya su tabbatar da cewa sun bada cikakken tsaro a jihohin su ta hanyar kula da ofisohin hukumar zaben da kuma kayan aikin da aka kawo domin gudanar da zaben yadda ya kamata.

Ya ce ya zama wajibi duk wani jami’in Dan sanda da ke kula da tsaron al’umma a yayin zaben da ya rika kula da yadda harkokin tsaron ke gudana, kuma da zarar sun samu wata matsala su sanar da ofisoshin yan’sanda da ke kusa dasu.

Muhammed Adamu ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su kwantar da hankulan su tare da basu hadin kai a yayin da suke   gudanar da ayyukan su a lokutan zabe.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!