Connect with us

Labarai

Rundunar yan sanda ta bada umarnin janye jami’anta daga kare manyan mutane

Published

on

Babban Sufeton  ‘yan sandan kasar nan Kayode Egbetokun,  ya ba da umarnin  janye jami’an ‘yan sandan ko ta kwana na kwantar da tarzoma wato  MOPOL daga  kare manyan mutane (VIPs). kamar yadda aka sanar a shafin rundunar na X. 

Shafin X, na rundunar  ya tabbatar dacewa Kayode Egbetokun ya bayyana haka ne a hedikwatar rundunar da ke birnin tarayya  Abuja yayin wata ganawar gaggawa da ya yi da kwamandojin rundunar ta Mopol. 

Ganawar ta biyo bayan cece-kucen da ya barke kan wani faifan bidiyo da ya nuna wani dan kasar China yana ba jami’an na Mopol  kudi a bainar jama’a, da hakan ya sa rundunar ta gayyaci jami’an da aka gani a bidiyon domin amsa tambayoyi,  da ya ce an ɗauki matakin ladabtarwa a kansu. 

Kayode Egbetokun, ya nuna rashin jin dadin sa tare da sukar  kwamandojin rundunar ‘yan sandan ta MOPOL, bisa yadda suke tura jami’an sashen zuwa tsaron manyan mutane a kasar. 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!