Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rundunar ‘yan-sandan Najeriya ta tura dakarunta Jihar Benue domin dakile rikice-rikcen Jihar

Published

on

Rundunar ‘yan-sandan Najeriya ta tura dakarunta kwararru na musamman da aka raba zuwa rukunoni 15 zuwa Jihar Benue domin dakile rikice-rikcen da ke faruwa a Jihar.

Kwamishinan ‘yan-sandan Jihar ta Benue Fatai Owoseni ya bayyana cewa Babban Sufeton ‘yan-sandan kasar nan Ibrahim Idris ne ya bada umarnin girke jami’an, inda ya sanar da cewa sun ceto wani jami’insu da ya yi batan dabo lokacin da aka kai hari a  kananan hukumomin Yogbo da Guma a Jihar.

Ya kara da cewa an rarraba jami’an a yankunan Kwande da Agatu da Makurdi da Buruku da Katsina-Ala da Gwer ta Yamma da kua Vandeikya.

Haka zalika ya shaida cewa jami’an na su sun zamu zarafin fatattakar masu kai hare-haren inda zaman alfiya ya fara samuwa a Jihar Benue.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!