Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Shugaba Buhari zai kai ziyara jihar Nassarawa gobe don kawo karshen rikicin manoma da makiyaya

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kai ziyara jihar Nasarawa a gobe Talata a wani bangare na lalubo hanyoyin dakile rikicin manoma da makiyaya dake yawan aukuwa a yankin.

Wasu daga cikin Al’ummar jihar ta Nasarawa na ganin cewa ziyarar ta shugaban kasa zata taka muhimmiyar rawa wajen magance rikice-rikicen Fulani da Makiyaya.

Mataimakin gwamnan jihar ta Nasarawa kan harkokin matasa, dalibai da kungiyoyi masu zaman kansu Mr. Samuel Akala ya bayyana cewa ziyarar ta shugaba Buharin da kuma tattaunawa da masu ruwa da tsaki da shugabannin al’umma babban Al’amari ne da ka iya dawo da zaman lafiyar da aka rasa tsakanin manoma da makiyaya.

Ya kuma kara da cewa ya tabbatar da cewa shugaba Muhammadu Buhari na da masaniya kan hargitsin da ake samu a jihar kuma ya dauki matakan da suka kamata don haka yace ziyarar zata kuma kwantar da hankalin al’ummar jihar.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!