Connect with us

Labarai

Shettima zai wakilci shugaba Tinubu a taron majalisar dinkin duniya

Published

on

Mataimakin Shugaban ƙasa Kashim Shettima, zai wakilci Shugaba Bola Tinubu a taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 80 da za a gudanar a New York daga gobe Litinin 22 ga Satumba zuwa Lahadi 28 ga Satumban bana.

Mai bai wa mataimakin shugaban ƙasa shawara kan harkokin yada labarai, Stanley Nkwocha, ya ce Shettima zai halarci taron tunawa da cikar Majalisar Dinkin Duniya shekaru 80, tare da shiga tattaunawar manyan shugabannin duniya.

A ranar Laraba 24 ga Satumba, Mataimakin Shugaban ƙasan zai gabatar da jawabin Najeriya a babban zauren Majalisar Dinkin Duniya, sannan ya halarci taron sauyin yanayi da Majalisar ta shirya, inda Najeriya za ta sanar da sabbin matakan kare muhalli karkashin yarjejeniyar Paris.

Shettima zai kuma shiga taron koli kan samar da gidaje masu araha da shugaban Kenya zai jagoranta, kafin ya wuce birnin Frankfurt da ke ƙasar Jamus don ganawa da jami’an bankin Deutche kafin dawowa gida Najeriya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!