Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Shugaba Buhari ya ce zai mayar da hankali wajen inganta rayuwar yan Najeriya

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce a sabon wa’adin mulkin sa na shekara hudu masu zuwa, zai mayar da hankali ne wajen inganta rayuwar jama’a ta bangare bunkasa ilimi da harkar lafiya.

 

Shugaban kasar wanda mataimakin sa Farfesa Yemo Osinbajo ya wakilta, ya bayyana hakan ne yayin bikin cikar jami’ar Lagos shekaru hamsin da kafuwa.

 

Ya ce yaki da fatara da cin hanci da rashawa da samar da aikiyin yi da kuma bin ka’idojin doka na daga cikin bangarori da gwamnati za ta mai da hankali wajen ganin ta kai kasar nan ga tudun mun tsira.

 

Ya ce gwamnati ta damu matuka kan tafiyar hawainiya da ake samu a bangaren ilimi da harkar lafiya, a don haka ta ga ya zama wajibi ta zage dantse wajen samun nasara a wa’adinta na biyu.

 

A cewar Farfesa Yemi Osinbajo muhimmancin da harkar samar da abubuwan more rayuwa ke da shi ga ci gaban kowace al’umma, ya sa gwamnati ta dauki gabaran gina sabbin tituna da sabunta wadanda ta gada da shimfida layukan dogo domin bunkasa tattalin arzikin kasar nan

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!