Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Shugaba Buhari ya dawo gida bayan halarta taron dumamar yanayi na COP24 a kasar Poland

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dawo gida Najeriya bayan halartar wani taron majalisar dinkin duniya kan dumamar yanayi mai taken: ‘’’COP24’’ a birnin Kotowice da ke kasar Poland.

 

Yayin taron na kwanaki goma sha biyu, shugaban kasar ya kuma gabatar da jawabi tare da tattaunawa da wasu shugabannin kasashen duniya da kuma al’ummar kasar nan mazauna kasar ta Poland.

 

Wasu daga cikin shugabannin kasashen duniyar da shugaba Buhari ya zanta da su, sun hada da: Alain Berset na kasar Switzerland da Andrzej Duda na kasar Poland da kuma shugaba Alexander Van der Bellen na kasar Austria.

 

A shekaran jiya talata ne kuma shugaba Buhari ya ziyarci gidan ajiya kayan tarihi na mutanen da suka rasa rayukansu a yakin duniya na biyu da ke Oswiecim.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!