Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Shugaba Buhari yayi ganawar sirri da jagoran jam’iyyar APC

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buharin ya yi ganawar sirri da jagoran jam’iyyar APC Asiwaju Bola Tinubu a jiya Laraba a fadar sa da ke Abuja.

Jagoran jam’iyyar ta APC Asiwaju Bola Tinubu ya isa fadar shugaban kasa da misalign karfe 4 na yammacin jiyan.

Sai dai kawo kammala ganawar sirrin a jiya ba’a bayyana wa manema labarai mainene makasudun ganawar ta su ba.

Amma kuma ana hasashen cewar ganawar ba zata rasa nasaba da shiga tsakani da shugaban kasa Muhamamdu Bauhari yayi kan rikicin da ‘ya’yan jam’iyyar ta APC suka fada tun bayan kammala zaben fidda gwani a sassan kasar nan.

Rahotanni sun bayyana cewar, ganawar ta su ta dauki lokaci, kuma ya zo dai-dai da kasa da awanni 24 da shugaban yayi liyafar cin abincin dare da ‘yan takarar da aka batawa a yayin zaben na fidda gwani.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!