Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu na hanyar dawowa Najeriya

Published

on

Shugaban kasa Bola Tinubu zai dawo Najeriya yau Talata bayan kammala hutunsa a ƙasashen Birtaniya da Faransa.

Ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa Bayo Onanuga, ya fitar ya ce, Tinubu zai koma domin ci gaba da ayyukansa daga ranar 16 gwatan Satumba.

A makon da ya gabata ne Tinubu ya halarci liyafar cin abincin dare tare da takwaransa na Faransa, Emmanuel Macron, a fadar Élysée da ke birnin Paris.

Sanarwar ta ce shugabannin biyu sun tattauna batutuwan ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin Najeriya da Faransa domin ci gaban ƙasashen biyu.

A ranar 4 ga watan Satumba ne Tinubu ya fara hutun na kwanakin aiki 10, a wani ɓangare na hutunsa na shekara da doka ta tanadar masa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!