Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu na shirin yin ganawar  gaggawa da manyan hafsoshin tsaro

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, na shirin yin ganawar  gaggawa da manyan hafsoshin tsaro dangane da  halin da ake ciki na matsalar tsaro a wasu jihohin kasar nan.

Wasu majiyoyi daga fadar shugaban kasa, sun tabbatar da cewa shugaba Tinubu zai gana da hafsoshin tsaro da kuma ministoci domin duba yadda za a magance matsalar tsaro, musamman a jihohin Filato, Benue da kuma Borno. 

Ta cikin wani sako da ya wallafa a kafar sada zumunta, Hadimin shugaban kasa, Daniel Bwala, ya zargi wasu gwamnoni da rashin yin amfani da kudaden harkar tsaro yadda ya kamata, duk da cewa suna karɓar makudan kudi a kowanne  wata.

Haka kuma, Bwala ya bukaci gwamnonin da su kafa rundunonin tsaron yankuna a matakin kananan hukumomi da gundumomi domin tattara bayanan sirri da dakile hare-haren da suka zama ruwan dare.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!