Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya amince da kafa tawagar da za ta yi aikin haɗin gwiwa da Amurka

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya amince da kafa tawagar Najeriya da za ta shiga wajen aikin haɗin gwiwa da Amurka, a karkashin kwamitin US Nigeria Joint Working Group, domin ƙarfafa dangantaka kan lamurran tsaro.

 

A cewar fadar shugaban kasa, wannan mataki na zuwa ne domin tabbatar da an samu tsari mai kyau na musayar bayanan sirri, horar da jami’an tsaro, da kuma ƙarfafa yaki da ayyukan ta’addanci a sassan ƙasar nan.

 

Haka kuma rahotanni sun bayyana cewa, tawagar za ta haɗa manyan jami’an tsaro, masu ba da shawara kan harkokin diflomasiyya, da kwararru a bangaren leken asiri, domin tabbatar da an cika manufofin haɗin gwiwar yadda ya kamata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!