Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya gana da Gwamna Fubara a Abuja

Published

on

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya gana da Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara, a fadar mulki ta Aso Villa da ke Abuja.

 

Rahotonni sun bayyana cewa, Fubara ya isa Aso Villa da misalin ƙarfe 6:20 na yamma, inda kai tsaye ya shiga ofishin shugaban ƙasa domin yin ganawar  sirri.

 

Wannan shi ne karo na farko da Fubara  gana da shugaba Tinubu tun bayan dawo da shi ofis, bayan watanni shida na dakatarwa da gwamnatin tarayya ta yi masa tare da ayyana dokar ta baci a Jihar Rivers, wadda daga bisani aka soke ta a ranar 18 ga Satumba, 2025.

 

Sai dai bayan kammala ganawar tasu ba a bayyana batutuwan da suka tattauna ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!