Labarai
Shugaba Tinubu, ya jaddada kudurinsa na kafa ‘yan sandan jihohi

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sake bayyana kudurinsa na kafa rundunar ‘yan sandan jihohi domin dakile matsalar rashin tsaro da ke addabar sassa daban-daban na Najeriya.
Shugaban ya bayyana hakan ne a daren ranar Litinin yayin da ya karbi bakuncin gwamnonin jihohi domin buda baki na hadin gwiwa a Fadar Shugaban kasa da ke Abuja, a wani taro na addinai biyu da ya hada azumin Ramadan da kuma lokacin Azumi na Kiristoci.
Tinubu ya jaddada cewa, gwamnatinsa ba za ta jinkirta cika alkawurran da ta dauka wa ‘yan Najeriya ba, tun kafin hawanta mulki a 2023.
You must be logged in to post a comment Login