Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya kira taron gaggawa na Majalisar ƙoli

Published

on

Shugaban Bola Ahmad Tinubu ya kira taron gaggawa na Majalisar ƙoli ta ƙasa da hukumar ƴan sanda a yau Alhamis, domin tattauawa kan matsalar rashin tsaro.

Wannan mataki na zuwa ne sakamakon yadda matsalar tsaro ke kara kamari a sassan kasar, musamman hare-hare, satar mutane da kuma rikice-rikice da ke addabar al’umma.

A cewar majiyoyi daga fadar shugaban kasa, za a tattauna kan yadda gwamnati za ta kara karfafa jami’an tsaro tare da samar da sabbin dabaru wajen yaki da ayyukan ta’addanci da rashin tsaro. Taron zai kuma duba batutuwan da suka shafi ci gaban tattalin arziki da kyautata rayuwar ‘yan kasa.

Majalisar ƙoli ta ƙasa na kunshe da tsoffin shugabannin ƙasa da gwamnonin jihohi da manyan jami’an gwamnati. Ana sa ran wannan taro zai samar da muhimman shawarwari da za su taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a Najeriya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!