Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu zai tafi Turkiyya ranar Litinin

Published

on

Shugaban Kasa  Bola Tinubu zai bar Abuja a yau  Litinin  don ziyarar aiki a turkiyya  , a wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa dangantakar ƙasashen biyu.

 

Hakan na cikin wata sanarwa da mai taimakawa shugaban kasa kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga ya fitar ga manema labarai.

 

Sanarwar ta ce ziyarar zata  mayar da hankali wajen hadin gwiwa a bangaren tsaro, ilimi, ci gaban zamantakewa, kirkire-kirkire, da kuma harkokin jiragen sama.

 

A  ziyarar Shugaba Tinubu, ana sa ran ƙasashen biyu za su gudanar da shawarwari na siyasa da diflomasiyya, waɗanda suka mayar da hankali kan muradun da suka shafi kuɗi, sadarwa, ciniki, da saka hannun jari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!