Connect with us

Labarai

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya dawo Najeriya

Published

on

A yau Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya sauka a Abuja, bayan wata huldar diflomasiyya a Japan da Brazil.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun Tinubu, Bayo Onanuga, ya fitar jirgin shugaban kasa, wanda ya tashi daga sansanin sojojin sama na kasa da kasa na Brasília da karfe 12:57 na rana a agogon Najeriya ranar Laraba, ya iso da sanyin safiyar yau Alhamis.

Tinubu ya halarci bukin budewa da cikakken taron bunƙasa nahiyar Afirka mai karo na 9 mai taken Tokyo International Conference on African Development (TICAD9) a ranar 20 ga Agusta a Japan.

Ya gudanar da tarurrukan kasashen biyu kuma ya kammala taron tattaunawa da al’ummar Najeriya.

Bayan kammala TICAD 9, ya bar Yokohama Inda ya tsaya a birnin Los Angeles NA Amurka, daga bisani ya wuce birnin Brasília.

A Brazil, ya gana da shugaban kasar Luiz Inácio Lula da Silva da manyan jami’an Brazil.

Shugabannin biyu sun yi wata tattaunawa ta sirri tare da rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna guda biyar.

Yarjejeniyar ta shafi harkokin sufurin jiragen sama da harkokin waje da kimiyya da fasaha da kuma noma da ma muhimman sassa a cikin tsarin ci gaban Najeriya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!