Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Shugaba Buhari ya mika da sakon ta’aziyya ga gwamnati da a’ummar jihar Nassarawa bisa ga gobarar iskar gas

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika da sakon ta’aziyar sa ga gwamnati da al’ummar jihar Nassarawa bisa ga gobarar da ta tashi a wata cibiyar sarrafa iskar gas da ke daf da wani gidan mai da ke garin Lafiya a jihar ta Nassarawa wadda ta yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai Malam Garba Shehu.

Sanarwar ta ruwaito shugaba Buhari na nuna damuwar sa matuka kan irin adadin mutanen da suka rasa rayukan su a dalilin hatsarin, inda mutane goma suka mutu wasu talatin suka jikkata ba ya ga motoci da shaguna da dama da suka kone.

Shugaba Buhari ta cikin sanarwar dai ya kuma mika sakon ta’aziyar sa ga iyalai da kuma ‘yan uwan wadanda suka rasa rayukan su.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!