Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kungiyar ECOWAS ta koka kan yaduwar kananan makamai sama da miliyan 10 a yammacin afurka

Published

on

Kungiyar raya tattalin arzikin yammacin afurka wato (ECOWAS), ta ce, kananan makamai sama da miliyan goma ne ke hannun jama’a ba bisa ka’ida ba a yankin na yammacin afurka.

Shugaban sakatariyar kungiyar Mr. Jean Claude Brou ne ya bayyana haka ga manema labarai yayin wani taro kan yankin Sahel.

Jean Claude Brou wanda kwamishina mai kula da harkokin siyasa, tsaro da zaman lafiya Francis Behanzin ya wakilta, ya ce, wajibi ne hukumomin da lamarin ya shafa su dauki mataki don dakile ci gaba da yaduwar su.

Ya kuma alakanta yawaitar makamai a hannun jama’a ba bisa ka’ida ba, da cewa, shine sanadiyyar rikice-rikice da kashe-kashen ta’addanci da ake samu a yankin.

Shugaban sakatariyar kungiyar ta ECOWAS ya kara da cewa, rashin ci gaban kasashen yankin musamman rashin aikin yi da ya yi katutu tsakanin matasa da kuma karin adadin jama’a da ke karuwa, yana kara ta’azzara matsalar rashin tsaro a yankin na yammacin afurka.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!