Connect with us

Labarai

Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda tare da lalata cibiyar kera bama-bamai a Zamfara

Published

on

Rundunar sojojin saman kasar nan NAF ta  Operation Fansa Yamma, ta hallaka  ’yan ta’adda da dama tare da lalata cibiyar kera bama-bamai da sansanonin su a jihar Zamfara.

 

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun sojojin saman, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya fitar a baya baya nan.

 

A cewar sa rundunar ta gudanar da hare-haren sama guda biyu masu tasiri a Dutsen Turba da kuma sansanin Kachalla Dogo Sule.

 

Dukkanin hare-haren an kai su ne a karamar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara, da aka kashe ’yan ta’adda da dama.

 

Air Commodore Ejodame ya ce bangaren sama na rundunar, bisa samun  sahihan bayanan sirri daga tushe daban-daban, ta tura jiragen yakin NAF domin kai farmaki kan maboyar ’yan ta’adda a wuraren da aka gano. 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!