Connect with us

Labarai

Sojoji sun kashe yan ta’adda 16 tare da kwato mutune 11 da aka sace

Published

on

Dakarun Rundunar sojin Najeriya, sun hallaka yan ta’adda 16 tare da kwato mutune 11 da aka sace a yankin arewa maso gabashin kasar nan

Dakarun sun yi karam batta da ƴan ta’addan ne a yankin Gidan Kaji kan titin Maiduguri zuwa Damboa, inda suka kashe 16 daga cikinsu, abinda ya tilasta wa da dama tserewa da raunuka.

Sojin sun kuma ƙwato kekuna 20, da makamai da sauran kayayyaki da suke amfani dasu wajen kai hari.

Cikin sanarwar da jami’in yaɗa labaran rundunar haɗin gwiwar  Operation Hadin Kai, Laftanar Kanal Sani Uba, ya fitar a jiya Laraba, ya ce cikin ayyukan da suka gudanar har da daƙile harin mayaƙan ISWAP kan sansanin soji.

A cewarsa, sojin sun kuma kama wasu da ake zargin na safarar kayayyaki ga mayaƙan ISWAP, inda aka same su da ƙwayoyi da suka tsara kai wa ƴan ta’addan a yakin Bukarti.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!