Connect with us

Labarai

Sojoji sun kwato bindigogi shida a hannun wanda ake zargi da safarar su a Taraba

Published

on

Rundunar  Sojin kasar nan karkashin runduna ta 6 ta  Operation Whirl Stroke ta tabbatar da kama wani mutum mai suna Abubakar Ibrahim mai shekaru 48 bisa zargin safarar makamai a Karamar Hukumar Ibi ta Jihar Taraba.

 

Hakan  na cikin sanarwar da Mukaddashin Mataimakin Daraktan Hulda da Jama’a na rundunar, Laftanar Umar Muhammad, ya fitar a jiya Asabar.

 

Sanarwar ta bayyana cewa jami’an da ke sansanin Forward Operating Base a Wukari ne suka kama shi bayan samun sahihan bayanan sirri, inda suka kwato bindigogi kirar PKT guda shida, harsasai kirar 7.62mm guda biyu, kudi Naira 170,000, mota kirar Peugeot 504 da wayar hannu.

 

Rundunar ta ce ana ci gaba da bincike kan wanda ake zargin, da ta ce  nasarar ta taimaka wajen dakile yaduwar makamai ba bisa ka’ida ba a jihar.

 

Shugaban runduna ta 6, Birgediya Janar Chukwuemeka Micheal Akaliro, ya yabawa sojojin kan yadda suka gudanar da aikin, tare da kira ga jama’a su ci gaba da bayar da sahihan bayanai ga hukumomin tsaro

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!