Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Tattalin arziki: Buhari ya isa ƙasar Saudiyya

Published

on

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya isa birnin Riyadh na ƙasar Saudi Arabia.

Shugaba Buhari ya isa birnin ne don halartar taron zuba hannun jari karo na biyar.

Rahotanni sun bayyana cewa shugaban ya sauka a filin jirgin saman sarki Khalid a birnin Riyadh da misalin ƙarfe 11 na dare.

Haka zalika ya samu tarba daga tawagar gwamnati da jakadancin ƙasar, baya ga tawagar rakiyar sa da suka haɗar da ministoci da sauran ƴan Najeriya mazauna Saudi Arabia.

Tuni dai sanarwar da mai magana da yawun shugaba Buhari, Malam Garba Shehu ya fitar, ta bayyana cewa shugaba Buhari zai gabatar da ibadar Umara gabanin dawowar sa gida bayan kammala taron.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!