Connect with us

Labarai

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kaso 4.23- NBS

Published

on

Hukumar kididdiga ta Najeriya NBS, ta bayyana cewa,  tattalin arzikin kasar ya ƙaru da kaso 4 da digo 23 cikin ɗari a ma’aunin tattalin arziki  a zango na biyu na shekarar nan da muke ciki ta 2025 idan aka kwatanta da shekarar 2024.

Hukumar ta bayyana haka ne ta cikin rahoton ta na  zango na biyu na shekarar 2025 da ta fitar a birnin tarayya a Abuja ,a  baya bayan nan.

A cewar rahoton, bangaren noma ya samu ci gaba  da kaso sama da 2,  idan aka kwatanta da kaso  2 da digo 60 da aka samu a zango na biyu na 2024, ya yin da  bangaren masana’antu ya samu ci gaban kaso  7 da digo 45, wanda ya ninka kaso  3 da digo 72 da aka samu a zango na biyu na 2024, sai bangaren ayyuka kuma ya samu kaso  3 da digo 94 idan aka kwatanta da 3 da 83 na zango na biyu na 2024.

NBS ta ce  a cikin zango na biyu na 2025, darajar kudaden shiga  ta kai Naira tiriliyan 100 da digo 73, idan aka kwatanta da Naira tiriliyan 84 da digo 48 da aka samu a zango na biyu na 2024, wanda ya nuna ci gaban shekara zuwa shekara da kaso  19 da digo 23.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!