Connect with us

Labarai

Tawagar wakilan Amurka ta iso Najeriya domin bincike kan iƙirarin kisan Kiristoci

Published

on

Tawagar ‘yanmajalisar Amurka ta iso nan Najeriya a yau Lahadi domin bincike kan sahihancin iƙirarin yi iwa Kiristoci kisan gilla.

mai bai wa  shugaban Najeriya shawara kan tsaro malam Nuhu Ribadu ya ce,  ya gana da wakilan kuma zuwan tawagar na cikin abubuwan da suka amince da shi a tasu ziyarar da suka kai birnin Washington a watan Nuwamba da ya gabata.

“Tawagar ta ƙunshi ‘yanmajalisar wakilai Mario Díaz-Balart, Norma Torres, Scott Franklin, Juan Ciscomani, da Riley M. Moore,” in ji Ribadu cikin wata sanarwa a shafinsa na sada zumunta.

Kazalika, Jakadan Amurka a Najeriya Richard Mills na cikin tawagar.

Ribadu ya ce sun tattauna matakan yaƙi da ta’addanaci, da zaman lafiya a Afirka, da hanyoyin ƙarfafa ƙawancen tsaro tsakanin Najeriya da Amurka

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!