Connect with us

Labarai

Tinubu ya ba da umarnin tsaurara matakan tsaro a wasu jihohi

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin karin tsaurara matakan tsaro a manyan yankunan dazuka na jihohin Kwara, Neja da Kebbi sakamakon karin garkuwa da mutane da hare-haren ’yan ta’adda da aka samu a kwanakin nan.

 

Jaridar The Nation ta rawaito cewa, a ƙarƙashin sabon umarnin, Rundunar Sojin Sama ta kasa za ta fara gudanar da tsaron sama na awa 24 ba tare da yankewa ba, a cikin zurfin dazukan wadannan jihohi, inda hukumomin tsaro suka nuna cewa su ne manyan mafakar kungiyoyin ta’addanci da masu garkuwa da mutane.

 

Ana sa ran hukumomin tsaro za su yi aiki tare domin binciko maboyar ’yan bindiga, hana motsin kungiyoyin ta’addanci a yankunan, tallafa wa sojojin kasa wajen kai farmaki da kuma kwato wuraren da aka mamaye.

 

Wannan mataki na zuwa ne yayin da alumma ke ci gaba da nuna damuwa kan yawaitar sace-sace da hare-hare a arewa ta tsakiya da arewa maso Yamma a kwanakin nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!