Connect with us

Labarai

Tinubu ya bai wa Shettima umarnin zuwa Birtaniya domin dauko gawar Buhari

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci mataimakinsa, Kashim Shettima, da ya tafi Birtaniya domin ɗauko gawar tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari zuwa Najeriya, bayan rasuwarsa a London.

 

Hakan na cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan kafafen yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya fitar a yau Lahadi 

 

Sanarwar ta bayyana cewa Buhari ya rasu ne da misalin ƙarfe 4:30 na yamma a wani asibiti da ke birnin London, bayan doguwar jinya. 

 

Tinubu ya ce ya tuntubi uwargidan marigayin, Hajiya Aisha Buhari, inda ya miƙa ta’aziyya da gaisuwar juyayi ga iyalinsa da kuma al’ummar Najeriya gaba ɗaya.

 

An kuma bayyana cewa daga yau tutocin Najeriya za su rika sauka rabin sanda a manyan wuraren gwamnati a matsayin girmamawa ga marigayin shugaban.

 

Marigayi shugaba Buhari ya mulki kasar nan sau biyu daga 1984 zuwa 1985 a matsayin shugaban mulkin soja, sannan aka sake zaɓensa shugaban ƙasa a jamhuriyya ta huɗu a shekarar 2015 da kuma 2019 a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!