Connect with us

Labarai

Tinubu ya karbi rahoton DSS kan batun satar dalibai

Published

on

Shugaban hukumar tsaro ta farin kaya DSS  ya kai wa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu rahoton halin da ake ciki game da sace-sacen ɗalibai da ‘yanbindiga suka yi a jihohin Kebbi da Neja da ke arewacin ƙasar.

 

Wata sanarwa da Bayo Onanuga, mai magana da yawun Tinubu, ya fitar ta ce shugaban DSS, Tosin Adeola Ajayi, ya gana da Tinubu ne a jiya Juma’a da dare.

 

A ranar Litinin ne ‘yanbindiga suka sace ɗalibai mata 25 daga wata sakandare a garin Maga da ke ƙaramar hukumar Danko-Wasagu a jihar Kebbi da ke arewa maso yamma.

 

Sai kuma ranar Juma’a wasu ‘yanbindiga suka sace ɗalibai fiye da 300 da malamansu a wata sakandaren da ke Papiri a cikin jihar Neja da ke tsakiyar Najeriya.

 

Tuni Tinubu ya soke balaguronsa zuwa taron G20 a Afirka ta Kudu saboda halin matsalar tsaron, kuma ya tura Ministan Tsaro Abubakar Badaru Neja, yayin da Ƙaramin Ministan Tsaro Bello Matawalle ya tafi Kebbi.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!