Connect with us

Labarai

Tinubu ya tura Kashim Shettima zuwa jihar Kebbi domin jajantawa al’ummar jihar

Published

on

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya tura mataimakinsa Kashim Shettima zuwa Jihar Kebbi domin jajanta wa gwamnatin jihar da iyayen daliban Makarantar sakandiren Maga da aka sace a farkon makonnan.

 

Hakan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga, ya fitar.

 

Sanarwar ta ce shugaban kasa ya nuna damuwa kan sace daliban, sannan ya bai wa hukumomin tsaro umarnin gaggawa domin ganin an ceto su cikin koshin lafiya.

 

Sanarwar ta kuma ce shugaban ya jajanta wa rundunar soji kan mutuwar jami’ansu Brigadier General Musa Uba a Borno yayin aiki.

 

Tinubu ya bukaci shugabannin al’umma da jama’a a yankunan da ake fama da matsalar tsaro da su rika taimakawa hukumomin tsaro da bayanai domin tabbatar da tsaron yankunansu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!