Connect with us

Labarai

Tinubu ya tura ministan tsaro Badaru Abubakar zuwa Naija in da aka sace dalibai sama da 200

Published

on

Gwamnatin Najeriya ta tura babban ministan tsaron ƙasar, Muhammad Badaru Abubakar, zuwa jihar Neja inda aka sace ɗalibai ‘fiye da 200’.

Ƙaramin ministan tsaron ƙasar, Muhammed Bello Matawalle ne ya bayyana haka ranar Juma’a da maraice a cikin shirin Ra’ayi Riga na BBC Hausa.

”Shi ma Badaru zai je Neja kamar yadda aka turoni Kebbi, domin ƙoƙarin gwamnati na kuɓutar da ɗaliban da aka sace”, in ji shi

Tuni dai Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya tura ƙaramin ministan tsaron zuwa jihar Kebbi – inda ƴanbindiga suka sace ɗalibai ƴanmata 25 – domin sanya idanu kan ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!