Connect with us

Labarai

Tinubu zai halarci taron zuba jari na ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje

Published

on

Shugaban ƙasa Tinubu, zai halarci taron zuba jari na Najeriya nan mazauna ƙasashen waje karo na takwas matsayin bako na musamman, wanda za a gudanar daga ranar 11 zuwa 13 ga watan Nuwamban 2025 a Abuja.

 

Shugabar hukumar kula da ’yan Nijeriya mazauna ƙetare NiDCOM’l, Abike Dabiri-Erewa ce ta sanar da hakan yayin taron manema labarai kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

 

Abike ta ce, tun bayan fara taron a 2018, an samu karuwar zuba jari daga ’yan Nijeriya da ke ƙasashen waje a fannoni kamar gidaje, kiwon lafiya, noma, fasahar sadarwa, makamashi, masana’antu da harkokin kirkire-kirkire.

 

Dabiri-Erewa ta kara bayyana cewa, a taron bara na 2024 an cimma yarjejeniyar zuba jari da ta kai kimanin naira miliyan 673 a fannoni daban-daban.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!